A jiya Alhamis ne aka rantsar da sabon shugaban kasar Burundi Evariste Ndayishimiye a filin wasa na Ingoma da ke birnin Gitegay, mako daya bayan mutuwar shugaba mai barin gado Pierre Nkurunziza ya yi.
An shirya rantsar da Ndayashimiye a watan Agusta amma Kotun Tsarin Mulki ta bada umurnin a rantsar da shi ba tare da bata locaci ba bayan mutuwar Shugaba mai barin gadon.
https://dimokuradiyya.com.ng/da-dumi-dumi-shugaban-kasar-burundi-ya-rasu/
Ndayashimiye ya zamo sabon shugaban Burundi ne yayin da ya samu kuri’u kaso 68 cikin 100 a zaben na watan Mayu wanda ya hana jam’iyyar adawa cika burinsu na ganin an soke zaben bisa zargin magudi.
Jam’iyyar CNDD-FDD ce ta zabi Ndayashimiye da ya gaji Nkurunziza kuma zai yi wa’adin shekara bakwai kafin sake tsayawa a zabe shi.