Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC) ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin satu biyu domin janye ƙarin farashin wutar lantarki da na man fetur da ta yi.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar bayan taro da masu ruwa da tsaki a ƙungiyar suka gabatar, wadda ta fitar a yammacin jiya laraba, mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa Kwamared Ayuba Wabba.
Jim kaɗan bayan sanarwar, Wabba ya zanta da manema inda ya ce, ɗaukar wannan mataki ya zama tilas.
A farkon watan Satumban da muke ciki ne dai gwamnatin tarayya ta yi ƙarin farashin wutar lantarki da kuma na man fetur wanda ya janyo cece-kuce a ƙasar nan.
Wasu a gefe kuwa musamman ‘yan jam’iyyar adawa na ganin cewa gwamnatin ta gaza ne shi yasa take amfani da yanayin da ake ciki domin ta nemi uzuri.