Ƴan bindiga sun hallaka Ƴan Sanda biyu a Enugu
Ƴan bindiga sun hallaka ƴan sanda guda biyu a ranar Alhamis wanda suka kai hari a wurin tsayawar ƴan sanda a Garriki, Akwuke ta Ƙaramar Hukumar Enugu ta Kudu a Jahar Enugu.
Majiyoyi sun ce Harbe-Harben da akayi ya sanya mazauna garin suka riga domin ceton rayukan su.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kotu ta yanke wa wasu ‘yan fashi da makami biyu hukuncin kisa a Akwa Ibom
A cikin saƙon karta kwana, majiyoyin wuce “akwai Harbe-harbe a Garriki yankin MTD sun Kashe mutane Ƴan Sanda biyu da wasu mutane.
Maharan sun je wurin da ƴan sandan suke da misalin ƙarfe 9:10 na safe.
Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar Daniel Ndukwe yace ƙwararrun Jami’ai na Rundunar tuni sun bi bayan ɓata garin.
Ndukwe ya ƙara dacewa “akwai Harbe-harbe a wurin da Ƴan Sanda ke tsayawa da bincike akan hanyar Agbani da safe kusa da hanyar Enugu/Port Harcourt, Kuma har yanzu ba’a gano sunayen su.
“Haka zalika, bayanan yadda lamarin ya faru har yanzu ba’a tabbatar dashi b, a yayinda Jami’an Rundunar tuni an tura su domin gano Ƴan Ta’addan. Za’a sanar da cigaban da aka samu.
Haka zalika, Rundunar Ƴan Sandan Jihar Rivers Eboka a ranar Juma’a, ya bada umarni da’a tura Jami’ai da yawa ya zuwa Ƙaramar Hukumar Oyigbo ta Jahar, domin gano Ƴan Ta’addan wanda suka kashe jami’an Ƴan Sandan.
Kwamishinan Ƴan Sandan ya bada umarnin a ranar Alhamis, bayan Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Grace Iringe-Koko ya Sanya hannu.