Ƴan Bindiga sun hallaka Ma’aikacin Kwalejin Kimiyya ta Zamfara, sun binne shi, bayan amshe 4M
Wasu Ƴan Bindiga sun hallaka wani ma’aikaci a sashen harkokin Ɗalibai dake a Kwalejin kimiyya da Fasaha ta Abdu Gusau Sanusi Haliru, bayan sun karɓi Naira Miliyan 4 daga iyalan sa.
Haliru dai sun sace shi akan hanyar Abuja-Kaduna a lokacin da yake hanyar halartar wani shiri na bita akan Shirin masu yiwa Ƙasa Hidima a Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan sanda Sun Bindige Dan bindiga Sanye Da Kakin Soji A Kaduna
Ƴan bindigar sun buƙaci da a biya su Naira miliyan 4, amma kuɗin basu kai ba a lokacin da suka buƙata.
Wani Makusancin mamacin Mohammed Nasir yace bayan sun tara Miliyan 4, iyalan sun kira suji ina zasu biya kuɗin fansar.
“Shugaban tawagar ƴan bindigar ya gaya mana wurin da zamu ajiye, inda ya gaya mana cewa wani zaizo ya karɓa.
“Bayan munje wurin bamu ga kowa ba.
“Kawai sai muka ga wasu mutane sun taho daga inda muke, inda suka yi gaggawar bincikar damu basu kuɗin.
“Sai muka miƙa kuɗin a garesu, sai ɗaya ya gaya mana cewa ɗan uwan mu ya daɗe da mutuwa.
“Mun buƙaci dasu bamu gawar shi domin yi mashi Sallah, abun baƙin ciki wai ya mutu kuma sun binne shi.
“Suka tafi cikin daji Maɓoyar mu, suka barmu cikin tashin hankali,” Inji Nasir.
Comments 1