Wani Ɗan Jarida mai aiki da Gidan Rediyo da Talabijin a Gusau Kwamared Idris Haruna Magami ya shiga hannun masu garkuwa da mutane.
A cewar shaidar Gani da Ido, An sace Magami akan hanyar Gusau Ɗansadau a lokacin da yake kan hanyar sa ta zuwa garin su Magami, kilomita 40 daga Gusau, Babban Birnin Jahar bayan ya tashi daga aiki.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamnan Cross River Ayade ya kori Sarki kan halartar taron PDP
Kwamared Magami ya kasance sanannen Ɗan Jarida ne a Gidan Rediyo da Talabijin na Zamfara, musamman a shirin shi dayake gudanarwa na Hausa mai suna “Su duniya manya”.
A cewar Ɗan Asalin garin Magami Malam Almu “Idris Haruna Magami yana kan hanyar sa ta zuwa garin su tare da abokin sa, Alhaji Kabiru a lokacin da aka kaiwa Abun Hawan su hari.”
Almu ya bayyana cewar Alhaji Kabiru ya samu nasarar tserewa , a yayinda ƴan bindiga suka sace Idris Magami tare da tafiya dashi inda ba’a ida sani ba.
A cewar sa, tuni ƴan bindigar sun yi magana da iyalan Idris Haruna, amma har yanzu basu faɗi ko nawa suke buƙatar a biya su a matsayin kuɗin fansa.
Haka zalika, dukkanin wani yunƙuri na yin magana da Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar Zamfara SP Mohammed Shehu bai samu ba a yayinda ba’a samu layin shi ba.