Ƴan Bindiga sun saki Basaraken Filato, bayan kwanaki 3 da sace shi
Basaraken Panyam a Ƙaramar Hukumar Mango ta Jahar Filato Mai Martaba Aminu Derwan, wanda ƴan bindiga suka sace ya samu ƴan ci.
An gano cewa Hakimi an sake shi ne a ranar Laraba da daddare bayan ya shafe kwanaki uku a hannun wanda suka sace shi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Bamu da masaniyar zama da gwamnatin tarayya balle mu janye yajin aiki – ASUU
Mai magana da yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar Alabo Alfred ya Tabbatar da sakin Derwan ga Majiyar mu a ranar Alhamis a Jos.
Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar yace “dagaske, an sake shi. Ina godiya.
Shugaban Matasa na Al’ummar Panyam Philip Yakubu wanda ya tabbatar da sakin Basaraken yace Al’ummar yankin tuni sun fara murna akan sakin shi da aka yi daya watsu a daren jiya.
Yakubu yace “muna rawa da waka tun bayan da labarin sako shi ya watsu, amma gaskiya sun biya kuɗin fansa kafin a sako shi.
Awanni kaɗan bayan ƴan bindiga sun kama shi, sun tuntuɓi iyalan su, sannan sun buƙaci a biya Naira miliyan 150 kafin sakin sa
Comments 1