Wata ɗaliba dake karatun aikin jarida a kwalejin kimiyya da fasaha ta Jahar Delta Ogwashi-Uku da akafi sani da Chidinma, ta daɓawa saurayin ta wuƙa Daniel Johnson, a dalilin firar dandalin sadarwa ta Whatsapp da wata mace abokiyar sa.
Majiyar Jaridar Dimokuraɗiyya ta ruwaito cewar, ta daɓawa saurayin nata wuƙa a ranar Laraba, 27 ga watan Oktoba, amma dai ya rayu bayan wannan al’amari daya faru.
Dayake jawabi ga Manema labaru bayan ya warke daga lamarin, ya bayyana cewa budurwar sa ta duba saƙonni dake cikin WhatsApp ɗin a lokacin da yake barci, kafin ta daɓa mashi wuƙa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kungiyar CAN Ta Koka Yayin Da Daliban Makarantar Bethel Baptist Suka Kwashe Kwanaki 120 A Hannun ‘’Yan Fashi
Yace “ina barci ta duba waya ta. Ta duba saƙonnin WhatsApp nawa da wata yarinya. Sai tayi amfani da wuƙa wajen daɓa Mani a hannu na, na dama.
“Na tashi na nemi taimako. Maƙwabta na, suka zo suka ceceni. An kirawo ƴan sanda amma ta kai kanta ofishin ƴan sanda na Asaba. Amma nayi sa’a tunda ina raye.
A lokacin da aka tuntuɓe shi domin tabbatar da lamarin, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar Ƴan Sandan Jahar Delta DSP Bright Edafe, ya shaida cewa, har yanzu ba’a kawo rahoton lamarin ga hedikwatar rundunar ba, ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.