Ƴan Sanda Sun Gargaɗi Ɗalibai Kan Tashin hankali wajen warware al’amari
Kwamishinan Ƴan sandan jihar Neja, Monday Bala Kuryas, ya shawarci kungiyar dalibai ta kasa (NANS) da su rika tattaunawa a koda yaushe wajen warware matsaloli tare da gujewa duk wani abu da zai iya haifar da tashin hankali.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga sun Hallaka Ƴan Sanda 3 a Enugu
CP ya bada shawarar ne a lokacin ziyarar da sabon zababben shugaban NANS, Kwamaret Umar Faruk Lawal, da sauran membobin zartarwa a ofishinsa da ke Minna.
Ya bukaci daliban da su kara mayar da hankali kan karatunsu domin kammala karatunsu da sakamako mai kyau don samun ayyuka.
Kuryas ya jaddada bukatar yin aiki tare domin samar da zaman lafiya a tsakanin al’umma yayin da ya nuna damuwarsa kan kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, na yajin aiki tare da fata janye wa nan ba da dadewa ba.
Shugaban ‘yan sandan jihar ya ce, “Ina rokon ku da ku yi amfani da shirye-shiryen bayar da tallafin karatu cikin adalci kuma kada ku yi amfani da irin wannan gata saboda wasu. Muna godiya da goyon bayan gwamnati da dalibai wajen yaki da miyagun laifuka a jihar”.
Lawal a cikin jawabinsa ya ce kungiyar ta bayyana CP a matsayin abokantaka na dalibai da magabatansa wajen halartar al’amuran dalibai, wanda aka baje kolin ta hanyar karbar kungiyar cikin kankanin lokaci ba tare da takarda ba.
Shugaban daliban ya amince da cewa ‘yan sanda sun samar da kashi 95 cikin 100 na tsaro a yayin taron NANS da aka kammala a Abuja wanda ya samar da sabbin shugabannin.
A cewarsa, “muna fatan kara kulla alaka da ‘yan sanda, tun daga rundunar ‘yan sandan jihar Neja. A matsayin majalisar koli na wakilcin ɗalibai, akwai buƙatar samun ingantaccen haɗin gwiwa tsakanin ‘yan sanda da ƙungiyar ɗalibai don jagoranci, haɗin kai da kuma kare cibiyoyin karatun”.
Daga nan ne shugaban daliban ya yabawa kokarin CP da rundunar ‘yan sanda wajen magance ‘yan fashi da sauran miyagun laifuka a jihar, yayin da ya yi alkawarin tallafa wa ‘yan sanda da karin bayanai wajen magance kalubalen aikata laifuka.
A wani labarin kuma: 2023: Kana wasa da Wuta – Jigon PDP ya gargaɗi Atiku kan Wike
Gabanin zaben 2023, jigo a jam’iyyar PDP a jihar Ribas, Princewill Dike, ya gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Alhaji Atiku Abubakar, da cewa zai yi wasa da wuta idan har ya yanke shawarar yin watsi da bukatun Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike.
Dike ya kuma gargadi Atiku cewa mutanen da ke a kusa da shi da kuma kara matsawa tsohon mataimakin shugaban kasar lamba, tare da kiran Wike, wanda ya bayyana a matsayin ‘mai tara jama’a, su ke kai shi cikin rami.