Tsohon Mai Magana da Yawun Ƙungiyar Gangamin Yaƙin Neman Zaɓe na Atiku Abubakar a shekarar 2019 Prince Kassim Afegbua ya shawarci Jam’iyyar PDP data bada tikitin takara Shugaban Ƙasa ga yankin Kudu, maimakon baiwa Atiku sabudda Shekarun sa.
A cikin wata sanarwa mai taken, “2023: Atiku da Shekarun sa a Siyasa,” Tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jahar Edo yace Atiku ya kamata ya ajiye buƙatar tsayawar sa takarar shugaban Ƙasa, tare da goyon bayan ɗan takara daga yankin Kudu domin adalci.
KARANTA WANNAN LABARIN: Mutum Daya Ya Mutu, Uku Sun Jikkata A Wata Gobara A Asibitin Kasar Hungary
Yace abun bazaiyi dai-dai ba ga duk wani ɗan Arewa dazai nuna sha’awar neman takarar shugaban Ƙasa a shekarar 2023 a cikin Jam’iyyar PDP.
Ya shawarci Kwamitin Amintattu na Jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Shugaban Jam’iyyar PDP Dr. Iyorchia Ayu dasu duba yiwuwar fito da ɗan takara mai ƙarancin shekaru.
Sanarwar ta ƙara dacewa “da rashin ƙwazon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sakamakon shekaru, rashin iya mulki, zai zama abun cin mutunci ne Alhaji Atiku Abubakar ya cigaba da nuna sha’awar neman takarar shugaban Ƙasa a shekarar 2023 domin ya cimma shekarun ritaya.