Jam’iyyar APC mai mulki a kasar nan ta shiga cikin halin ruɗani dangane da nazarin yankin da zai ja ragamar shugabancinta na kasa da kuma.
Kazalika jam’iyyar ta gaza cimma matsaya dangane da wanene za ta tsaida shi takarar shugabancin kasar nan a zaben shekara ta 2023.
Majiyoyi da dama sun tabbatar da cewa wannan sa-toka-sa-katsi ne ya jinkirta gudanar da babban taronta na kasa wanda majalisar zartaswarta zai bayyana.
Kimanin sama da shekara guda kenan jam’iyyar ke gudanar da mulkin rikon kwarya karkashin gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni.
Kuma dai sau biyu kenan ana kara wa’adin jagorancin su bayan tuɓe majalisar Zartaswar da Kwamared Adams Oshiomole yake jagoranta a can baya.
Sai dai duk da haka, majiyoyi sun shaida cewa a yanzu haka ana harin kara wa’adin mulkin rikon kwaryar jam’iyyar da wata takwas.
Yanzu haka dai yadda tsarin yake, muddin arewacin kasar nan ya samar da shugaban jam’iyyar, to babu makawa kudanci ne zai samar da dan takarar shugabancin Kasa don gudun mai uwa a gindin murhu.