Daga: Abbas Yakubu Yaura
Dan takarar mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC, Kashim Shettima, ya bukaci jam’iyyar da ta hada kan Najeriya, ta kuma mai da ita abin alfahari ga bakar fata.
Shettima ya kara da cewa, ba mahara ne suka lalata Roma ba, sai dai yadda Romawa suka yi kasa a gwiwa, inda ya ce lokaci ya yi da za a rera wakokin hadin kai da zaman lafiya da wadata da kwanciyar hankali don ganin Najeriya ta samu ci gaba.
Tsohon gwamnan jihar Borno ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Abuja lokacin da Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na kasa ya gabatar da shi a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa a hukumance.
Ya ce, “A cikin makonni da watanni masu zuwa, dole ne mu shiga cikin ramuka, mu shiga lungu da sako don rera wakokin hadin kai, zaman lafiya, wadata da kwanciyar hankali.
“Bari mu hada kan kasar nan, mu maishe ta abin alfahari ga bakar fata.”
Shettima ya kuma bayyana Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a matsayin jigon siyasa da halin rashin son kai.