Kwamitin yakin neman zaben (PCC) a ranar Lahadi ta sanar da tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara, a matsayin mamba na kwamitin “nan ta ke“.
Babban Darakta na kwamitin jam’iyyar PDP a yakin neman zabe PCC, Aminu Tambuwal, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce nadin Dogara “yana daga cikin ayyukan da muke ci gaba da yi na hada kai da dan takararmu na shugaban kasa, Atiku Abubakar, domin mu maido da martabar babbar kasar mu Najeriya”.
KU KARANTA KUMA Wasu Jiga-jigan Jam’iyyar APC Sun Fice Daga Marawa Tinubu Baya, Sun Amince Da Atiku
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tattaro cewa, Dogara ya jagoranci gungun ‘ya’yan jam’iyyar APC arewa wajen daukar Atiku a matsayin dan takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Bogoro da Dass da Tafawa Balewa na tarayya ya yi Allah wadai da tikitin mabiya dan takarar APC Bola Tinubu da Kashim Shettima.
A Wani Labarin Kuma Sanata Uba Ya Bukaci Al’umma Su Kasamce Masu Kyawawan Dabi’u
Dan takarar gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya bukaci al’umma da su gyara halayensu yayin cudanya da sauran mutane sai an zama na gari.
Sanata Uba Sani ya yi wannan magana ne ya yin da halarci taron da kungiyar lauyoyi Musulmi ta kasa MULAN reshen jihar Kaduna ta shirya, wanda shi ne Bako na musamman.