Daga: Abbas Yakubu Yaura
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabi’u Kwankwaso, ya shawarci takwaran sa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da ya duba kansa.
Akwai damuwa game da lafiyar Tinubu tun bayan da ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/hanyoyin-sadarwar-kasar-canada-sun-gamu-da-wani-cikas/
Da yake magana a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise ranar Lahadi, Kwankwaso ya gargadi Tinubu da ya kula da lafiyarsa.
A cewar Kwankwaso, dambarwar yakin neman zabe na bukatar kokari matuka.
“Idan ka ga abokina, Bola, ka gaya masa ya sauƙaƙa, kula da lafiyarsa sosai kuma ka tabbatar da cewa… saboda ina ƙaunarsa sosai, abokina ne,” in ji shi.
“Wannan yakin yana da tsauri sosai, yana bukatar kokari sosai da dai sauransu.”
“Ina fatan zai ji sauki domin mu ci gaba da fafutukar tabbatar da kasa daya mai karfi da wadata a Najeriya,” inji shi.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito a ranar Lahadin da ta gabata ne Tinubu ya tabbatar da tsohon gwamnan Borno, Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa.
A Wani Labarin Kuma Rundunar ‘yan sandan jihar Legas na gudanar da bincike a kan lamarin mutuwar dalibai biyu a cikin wata motar bus din makaranta.
Yaran sun mutu ne a lokacin da suke dawowa daga makaranta a unguwar Aguda da ke Legas a ranar Juma’a, 8 ga watan Yuli, 2022.
An samu labarin cewa daliban sun yi ta kai karar direban motar Odunsa Mandala kan rashin jin dadi, amma an yi watsi da korafin nasu har sai da akasarin su suka shake wanda kuma suka rasa rayukan su a lokacin da yake daukar daliban zuwa gidajensu bayan tashi daga makaranta.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, SP Benjamin Hundeyin, ya ce: Eh, an kama direban amma daliban sun rasa ransu, abin bakin ciki. Wani direban bas na makaranta ya yi watsi da korafe-korafen yaran da ya kai gida cewa ba su da lafiya. Wasu daga cikin yaran sun sume, biyu daga ƙarshe sun mutu.
Makarantu suna buƙatar haɓaka wasan su a cikin daukar ma’aikata kuma su mai da hankali kan dacewa da aiki.
Iyaye suma suna buƙatar yin cikakken binciken makarantu da wuraren aiki kafin su ba wa yaran su kulawa.
A halin yanzu, an sanar da hukumar da ta dace game da wannan babban sakaci. Tsaro aikin kowa ne.”