2023: Kana wasa da Wuta – Jigon PDP ya gargaɗi Atiku kan Wike
Gabanin zaben 2023, jigo a jam’iyyar PDP a jihar Ribas, Princewill Dike, ya gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Alhaji Atiku Abubakar, da cewa zai yi wasa da wuta idan har ya yanke shawarar yin watsi da bukatun Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike.
Dike ya kuma gargadi Atiku cewa mutanen da ke a kusa da shi da kuma kara matsawa tsohon mataimakin shugaban kasar lamba, tare da kiran Wike, wanda ya bayyana a matsayin ‘mai tara jama’a, su ke kai shi cikin rami.
KARANTA WANNAN LABARIN: Tinubu, Atiku, Obi, Da Sauransu Zasu Biya Naira Milliyan 10 Kafin Lika Fastocinsu A Jihar Kogi
Ku tuna cewa PDP ta fada cikin rikicin siyasa tun bayan zaben fidda gwani na jam’iyyar, inda Wike da Atiku ke tsakiyar ta.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Dike ya yi imanin cewa Wike ya ci gaba da zama kashin bayan PDP, inda ya kara da cewa ya kamata Atiku da jam’iyyar su yi abin da ya dace ta hanyar sake fasalin jam’iyyar PDP domin bai wa ‘yan Kudu dama gabanin zaben badi.
Sanarwar Dike ta kara da cewa: “Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP zai yi wasa da wuta idan ya ga dama ya yi watsi da bukatun Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, da sansaninsa. Mutanen da ke rataye a kusa da shi kuma suna matsa masa lamba don ya kira bacin ran Gwamna Wike ya kai shi cikin rami.
A wani labarin kuma: Yanzu-Yanzu: Ƴan Bindiga sun Hallaka Ƴan Sanda 3 a Enugu
Wani hari da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai a daren Laraba, ya yi sanadin mutuwar ‘yan sanda akalla uku a jihar Enugu.
DAILY POST ta samu labarin lamarin ya faru ne a titin Chime Avenue, New Haven, karamar hukumar Enugu ta Arewa.