Tsohon dan takarar shugaban kasa, Pat Utomi, ya yi ikirarin cewa wasu tsoffin shugabannin kasa guda biyu magoya bayan dan takarar shugaban kasa ne na jam’iyyar Labour LP, Peter Obi.
Utomi ya bayyana haka ne a yayin da yake jawabi a wani taro a ranar Juma’a, wanda kungiyar Yell Out Nigeria for Good Governance ta shirya a Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yanzu-yanzu: Jam’iyyar PDP Tayi Rashin Dan Takarar Majalisar Wakilai
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta tattaro cewa Utomi bai bayyana sunayen tsoffin shugabannin kasar ba.
Amma Utomi ya lura cewa a shirye suke su yi wa Obi aiki, don ganin ya zama shugaban Najeriya na gaba.
A cewarsa, jam’iyyar APC da PDP ba su da wani tsari mai karfi kamar na jam’iyyar LP.
“Kudi kadai ba ya cin zabe. Tsofaffin shugabannin kasa guda biyu sun ce min su ‘Yan Uwa na ne.”
“Mutane da yawa suna son shiga harkar ne ba tare da sun shiga jam’iyyar Labour ba don tabbatar da cewa Peter Obi da Baba-Ahmed sun yi nasara, don haka za su iya kwace kasarmu daga hannun wadanda suka rike mu.”
“Jam’iyyar LP tana da mafi kyawun tsari fiye da PDP da APC.”
“Tsarin su wata ƙungiya ce ta masu laifi waɗanda za su iya gyara zaɓe. Dole ne mu daina cewa; hakan ba tsari bane,” in ji Utomi.
A wani labarin kuma, Sanata Uba Sani Ya Bada Tallafin Karatu Ga Wasu Dalibai A Jihar Kaduna
Sanatan Kaduna ta tsakiya wanda shi ne dan takarar gwamnan a jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya taya murna ga wadanda suka rabauta da tallafin karatu.
Uba Sani wanda ya raba tallafin ga wasu Dalibai a jihar ya bukace su da su zage damtse wajen yin karatu don amfanar da al’ummarsu.