By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, a ranar Laraba ta kama wasu ‘ya’ya biyu na wani jigo a jihar Ebonyi, Marigayi Sanata Office Nwali bisa zarginsu da kin sauka ga wani dan takara a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da aka kammala a jihar.
An tattara cewa, Barista Rollins Offa Nwali da dan uwansa Engr Alfred Offa Nwali a ranar Alhamis an kama su a Onueke dake karamar hukumar Ezza ta kudu a jihar.
FCTA Ta Sake Bude Kasuwar Sayar Da Kayayyakin Gini Ta Dei-dei
Rollins Offa Nwali, dan takara ne a zaben fidda gwani na majalisar wakilai ta APC.
Ya tsaya takarar kujerar mazabar Ezza ta kudu a jihar kafin a kama shi.
Wata majiya ta yi zargin cewa an kama Mista Offa Nwali ne saboda ya ki sauka daga mulki saboda abokin hamayyarsa a zaben.
“An kira shi da yawa daga gidan gwamnati don ya sauka amma ya shaida musu cewa a matsayinsa na dan daya daga cikin wadanda suka kafa jihar, abokin hamayya ne ya kamata ya sauka bashi ba.
“Ya sha fama da barazana da yawa kan zaben amma ya ki sauka daga mulki ya gwammace ya fita fagen daga. Sun kama shi ne saboda sun ga cewa zai yi nasara ne saboda yana da adadi mai yawa na mutane a mazabar,” inji majiyar.
Majiyar ta kuma yi zargin cewa an fatattaki magoya bayansa da suka hada da wasu daga cikin wakilai daga wurin zaben.
Dattijon ’yan’uwan biyu, Oguzor Offa Nwali ya tabbatar da kama ‘yan uwan.
Ya kuma yi zargin cewa “masu mulki” a jihar ne suka sa a kama shi domin ya share wa dan takarar da suke so ya yi nasara.
“Eh, an kama ‘yan uwana biyu kuma mun ji an kai su hedikwatar ‘yan sanda da ke Abakaliki”, in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Chris Anyanwu ba a samu jin ta bakinsa ba saboda layukan wayarsa a lokacin da ake gabatar da wannan rahoto suna kashe.