Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Kasa (NRC) za ta ci gaba da jigilar fasinjoji daga Abuja zuwa Kaduna ranar Litinin, inda za a dawo da jiragen kasa guda biyu kacal.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Manajin Darakta na Hukumar NRC, Fidet Okhiria ya aikewa gidan Talabijin na Channels a ranar Asabar.
Sanarwar ta nuna jirgi na farko zai tashi daga tashar jirgin kasa ta Rigasa a jihar Kaduna zuwa Abuja da karfe 8:00 na safe yayin da daga Abuja kuma jirgin na farko zai tashi daga tashar jirgin Idu zuwa jihar Kaduna da karfe 9:45 na safe.
KU KARANTA KUMA Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Zirga-zirgar Jirgin Kasan Kaduna-Abuja
Hukumar NRC ta kuma bayyana cewa, a wani bangare na sabbin matakan tsaro, a yanzu ya zama tilas fasinjoji su gabatar da lambar shaidarsu ta kasa da kuma ingantaccen tikitin shiga jirgi kafin a ba su izinin shiga.
Har ila yau, ya ce siyan tikiti ta hanyar wakili yana iyakance ga yara ƙanana da ƙayyadadden adadin fasinjoji manya.
Ana samun tikitin kan shafin intanet da manhajar hukumar daga karfe 8:00 na safe ranar Lahadi 4 ga watan Disamba, 2022 yayin da ofisoshin tikitin a tashoshin jirgin kasa za su bude daga karfe 6:30 na safe ranar Litinin 5 ga watan Disamba.
DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa NRC ta dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a kan hanyar bayan ‘yan ta’addar Boko Haram sun kai hari kan wani jirgin fasinja da ke tafiya Kaduna a ranar 28 ga Maris na 2022.
Maharan sun tarwatsa titin jirgin tare da jefa bama-bamai a cikin jirgin da ke tafiya, inda suka kashe wasu tare da yin awon gaba da fasinjoji sama da 60. Harin da ba a taba yin irinsa ba ya janyo cece-ku-ce tsakanin kasashen duniya da na kasa baki daya.
‘Yan ta’addan, wadanda suka kai hari kan jirgin kasan da ke kan hanyar Kaduna, sun sako mutanen da suka yi garkuwa da su a lungu-lungu inda aka sake sakin mutanen a ranar 5 ga Oktoba, 2022.
Kafin a sako mutanen da aka yi garkuwa da su gaba daya, ‘yan uwa da ke cikin rudani sun yi zanga-zangar neman a sako ‘yan uwansu.
A Wani Labarin Kuma ISBD Ta Bada Kwangilar Biliyan 1.87 Don Samar Da Mahautu Na Zamani A Kano
A kokarin da take yi na dakile shiga haduran da ke tattare da lafiyar al’umma, kungiyar noma da makiyaya ta jihar Kano, KSADP, ta bayar da kwangiloli a kan kudi Naira biliyan 1, 549, 000, 000 don inganta gidajen mahauta guda 20 a jihar Kano.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun Ameen K. Yassar.