• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Tuesday, February 7, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Tsaro

‘Yan bindiga sun kashe jumullar mutane 1,126 cikin watanni 6 – Cewar Ƙungiyar Amnesty International

abubakar by abubakar
August 24, 2020
in Tsaro
Reading Time: 2 mins read
0 0
0
0
SHARES
3
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Ƙungiyar kare hakkin ɗan-Adam ta ƙasa da ƙasa, Amnesty International ta ce ’yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 1,126 a ƙauyukan dake Arewacin Najeriya cikin watanni shidan farkon wannan shekara.

Ta ce kashe-kashen sun faru ne a jihohin Kaduna, Katsina, Neja, Filato, Sokoto, Taraba da kuma Zamfara, tare da zargin sojojin Najeriya da gaza kare su a yayin da hare-haren ƙungiyar Boko Haram ke ƙaruwa.

A sanarwa da ta fitar ranar Lahadi, Amnesty ta zargi mahukunta da rura wutar kashe-kashe da satar jama’a saboda gaza gurfanarwa da kuma hukunta masu aikata laifukan.

Ta kuma ce tana da cikakkun rahotannin cin zarafin manoma da ƙungiyoyin kare hakkin ɗan-Adam da ke yin kira ga gwamnati ta ɗauki matakan da suka dace.

“Rashin yin katabus daga jami’an tsaro wajen kare rayukan jama’a daga waɗannan hare-hare abun kunya ne matuka,” inji Daraktan Anmnesty a Najeriya, Osai Ojigho.

“Bugu da ƙari, jami’an tsaro na jan kafa wajen kai ɗauki ga jama’a bayan samun gargaɗi ko barazana daga mahara da kuma rashin hukunta waɗanda aka kama ya sa ’yan ƙauyukan sun rasa madafa”, inji ta.

Ƙungiyar ta yi zargin cewa yawanci maharan a kan babura ɗauke da muggan makamai kan yi wa ƙauyukan ƙawanya suna harbi kan mai uwa da wabi, su ƙona gidaje wuta, su sace dabbobi da amfanin gona da kuma mutane domin neman kuɗin fansa.

Ta ce aƙalla mutum 380 aka sace a jihohin Kaduna, Neja, Katsina, Nasarawa da Zamfara a 2020, yawancinsu mata da ƙananan yara.

http://dimokuradiyya.com.ng/amnesty-international-tayi-alawadai-da-kama-wanda-ya-haɗa-zanga-zanga-a-jihar-katsina/

Har wa yau, ’yan bindigar kan kashe iyalan da suka gaza biyan kuɗaɗen fansar da aka yanka musu.

Amnesty ta ce akwai wani hari da aka kai Unguwar Magaji a Jihar Kaduna amma ko da jami’an tsaro suka je wajen, da suka ga makaman maharan sun fi nasu sai suka juya, kafin su dawo kuma an kashe kusan mutum 17.

A Jihar Taraba kuwa, ƙungiyar ta ce aƙalla mutum 77 rikicin ƙabilanci tsakanin ƙabilun Tibi da Jukun ya hallaka.

A ranar 28 ga watan Mayu kaɗai, a cewar, harin ’yan bindiga ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 74 a ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto

A Katsina, rikicin ya yi sanadiyyar raba manoma da dama da gonakinsu da kuma iyalansu.

Kimanin mutum 33,130 ne a waɗannan jihohin yanzu suke zaune a sansanonin gudun hijira. Wasu kuma sun koma wurin ’yan uwa, yayin da dubban manoma kuma a bana ba za su iya noma gonakinsu ba.

Ƙungiyar ta yi kira ga mahukuntan Najeriya da su tashi tsaye wajen gudanar da bincike a kan kashe-kashen tare da hukunta waɗanda duk aka samu da laifi.

To sai dai da aka tuntuɓe shi a kan rahoton na Amnesty, Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya, Frank Mba bai cw komai ba game da lamarin.

Wannan ba shi ne karon farko da rahoton ƙungiyar ke zargi hukumomin Najeriya da gaza kare rayuka da dukiyoyin jama’a yayin waɗannan hare-haren ba.

Tags: Amnesty InternationalKadunakatsinaMatsalar TsaroNajeriyarundunar sojiRundunar yan sandaZamfara
Previous Post

Idan gwamnati na son mu janye yajin-aiki sai an cika mana buƙatunmu – Martanin ASUU ga Gwamnatin tarayya.

Next Post

Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekara 64 A Duniya

Next Post

Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekara 64 A Duniya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2328 shares
    Share 931 Tweet 582
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    1491 shares
    Share 596 Tweet 373
  • CBN Ya Sake Fitar Da Sabbin Bayani Kan Dawo Da Tsofaffin Takardun Kudin Naira

    1401 shares
    Share 560 Tweet 350
  • Rikicin Takara Gwamnan Adamawa A APC: Kotu Ta Tsayar Da Hukunci Kan Nuhu Ribadu Da Yake Yiwa Binani

    1051 shares
    Share 420 Tweet 263
  • Yan sanda a Katsina sun cafke yaro dan shekara 13 saboda ya kashe yan ta’adda

    991 shares
    Share 396 Tweet 248
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023
Shugaban INEC Ya Gana Da Emefiele Kan Sabbin Manufofin Kudin Naira

Shugaban INEC Ya Gana Da Emefiele Kan Sabbin Manufofin Kudin Naira

February 7, 2023
Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Ya Yi Babban Rashi

Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Ya Yi Babban Rashi

February 7, 2023
Rashin Tsaro: Shugaban INEC Ya Gana da NSA Gabanin Zaben 2023

Rashin Tsaro: Shugaban INEC Ya Gana da NSA Gabanin Zaben 2023

February 7, 2023
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5
Siyasa

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo
Labarai

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023
Labarai

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5
  • ‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo
  • NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In