Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ce yana jiran sakamakon binciken hatsarin jirgin da ya faɗi a rukunin wasu gidaje a Ikeja dake jihar Legas.
A sakon ta’aziyyarsa ga makusantan waɗanda hatsarin na ranar Juma’a ya ritsa da su, shugaban ya ce Najeriya gaba ɗaya na jiran hukumomin abin ya rataya wuyansu su gabatar da rohoton binciken.
Tuni hukumar binciken haɗarin jiragen Sama (AIB) ta ɗauki akwatin ɗaukar bayanan jirgin, bayan jami’an tsaro da na agaji sun ɗauke waɗanda hatsarin ya ritsa da su.
Haɗarin ya yi sanadiyyar mutuwar matuƙan jirgin mai saukar ungulu su biyu tare da jikkata mutum na uku da ke cikin jirgin wanda aka garzaya da shi asibiti, wanda shi ma daga baya rai ya yi halinsa.
https://dimokuradiyya.com.ng/mutum-ɗaya-ya-rasa-ransa-sakamakon-haɗarin-jirgin-sama/
Saƙon da kakakin shugaban ƙasa Femi Adesina ya fitar ya roƙa wa mamatan rahama da juriyar rashin ga ‘yan uwa da abokan arziƙi.
Rahotanni na cewa jirign ya faɗo kan wani gida a layin Salvation a unguwar Opebi da ke ƙaramar hukumar Ikeja.
Kakakin Hukumar Agaji na jihar Legas (LASEMA), Nosa Sokumba ya tabbatar da aukuwar haɗarin na ranar Juma’a wanda ya ritsa da jirgin kamfanin
“Tabbas jirgi mai saukar Ungulu ya faɗo da misalin 12 na rana a Opebi. Jami’an LASEMA na ƙoƙarin ba da agaji a wurin”, kamar yadda kakakin ya bayyana.