Hukumar ƙarɓar koke-koke da yaƙi da rashawa ta Kano ta ce ta yi iya ƙoƙarin ta wajen ganin ta magance ta’azzarar farashin shinkafa sai dai a wannan karon abin ya ci tura.
Shugaban hukumar Muhyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan, ta cikin shirin Inda Ranka na nan Freedom Radio, yana mai cewa, baza su iya daidaita farashin shinkafa ba a yanzu domin matsalar ba daga masu samar da shinkafar bane.
Ya ƙara da cewa hana shigowa da shinkafar da gwamnatin tarayya ta yi shi ne musabbabin da ya haifar da tsadar shinkafar, kuma gwamnatocin jihohi baza su iya taɓuka komai a kai ba.
“Gwamnatin tarayya ce kaɗai zata iya kawo ƙarshen matsalar ta hanyar bada dama a ci gaba da shigo da shinkafar kamar yadda ake shigowa da alkama” a cewarsa.
Mutane da dama na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu dangane da ƙarin farashin shinkafa wanda suke gane talaka ne zai kwana a ciki.