Gwamnan Jihar Kaduna Mallam Nasiru El-Rufai ya ce a tunaninsa kamata ya yi ace mulki ya koma yankin kudancin Najeriya a shekara ta 2023.
Gwamnan ya bayyana hakan ne aAa yayin hirarsahhirarsa dadda sashin HausayHausa na BBC, gwamnan yace babu wata doka da ta tanadi hakan amma yin hakan zai kyautatawa kowane ɓangare.
“Akwai tsarin da ake bi na karba-karba, inda kowa ya amince cewa idan Arewa ta yi mulki shekara takwas, Kudu za tayta mulki shekara takwas” cewar El-Rufa’i.
Ya ƙara da cewa, “Shi ya sa na fito na ce bayan Shugaba Buhari ya yi shekara takwas, kada wani ɗan Arewa ya nemi mukamin. A bar wa ‘yan kudu suma su samu shekara takwas”.
Sai dai El-Rufa’i ya ja hankalin wanda suke ganin cewar yana da sha’awar tsayawa takara, amma ya nuna bashi da ra’ayin hakan.
Ya ce, “Allah Shi Yake ba da mulki, ko kana so ko ba ka so idan yana so zai ba ka amma ni ban taɓa neman shugabancin Najeriya ba, ba wanda zai ce na taɓa nema,” El-Rufa’i ya bayyana.
Ko a kwanakin nan, kiran da wani makusancin Shugaba Buhari, Mamman Daura ya yi cewa lokaci ya yi na jingine yanki a bi cancanta wajen zaɓen magajin Buharin a 2023 ya tayar da ƙura.