Daga Abdullahi Kebbi
A kalla mutane 8 ne ake kyautata zaton sun rasa rayukansu sakamakon tashin Gobara a wata mahakar Ma’adanai a kasar Zimbabwe.
A wata sanarwa da ma’aikatar yada Labaran kasar Zimbabwe ta fitar tace ” lamarin ya faru ne a garin Mazowe inda ake Hakar Ma’adinai ta jumbo.
Ya zuwa wannan lokacin dai anyi nasarar ciro Gawarwakin wadanda lamarin ya shafa su 8, sannan ana kan bincike don ganin dalilin faruwar wannan lamari.