Daga Zahra Sarki
Gwamna Bala Muhammad Abdulkadir, na Jihar Bauchi, ya kai ziyarar gani da ido makarantar sakandire da ke karamar hukumar Katagun domin Gane ma Idon sa Halin da Makarantar ta Tsinci kanta daga Gwamnatin da ta Shude.
A ya yin Wannan Ziyarar Gwamnan ya samu zantawa da wasu daga cikin daliban Makarantar don jin matsalolinsu Ciki Har da wani Dalibi mai Suna Usman Muhammad, wanda shine shugaban daliban Makarantar Wato (Head Boy) a Turance.
Dalibin ya Fadawa Gwamnan cewa a Karkashin Bishiyoyi su ke karatu babu Kujerun zama babu kayan karatu kamar littafai, Alli, da kuma shi kansa dakin karatun, domin Wasu Dakunan Karatun duk Sun Rushe kuma Ba a Gyara ba.
Bayan jin Wadannan Koken da Gwamna ya yi ya Zagaya Ko’ina a Fadin Makarantar Inda daga Bisani Ya ce Za a Magance Kafatanin Matsalolin da Suka Addabi Fannin Ilimi a Yankin da ma Jihar Baki daya.