By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Alhamis din data gabata ne Sanata mai wakiltar Abia ta Kudu a majalisar dokokin kasar, Eyinaya Abaribe, ya yi kira ga daukacin wadanda suka yi rajista a jihar Anambra da su fito domin gudanar da ayyukansu na jama’a a wajen kada kuri’a ranar Asabar mai zuwa.
Abaribe ya bada wannan umarni ne bayan kungiyar Injiniyoyi ta Najeriya ta karrama shi a wani biki daya gudana.Abaribe ya kara da cewa, “Idan ba ku yi zabe ba, ku ma kun yi zabe kamar yadda kuka ba wa wadanda suka kada kuri’a damar zaben zabinsu.”
Tun da farko dai, ya dora laifin rashin lafiya a siyasar jihar kan hanyoyin da suka hada jihar Abia da jihohin dake makwabtaka da ita, inda yace babu ruwanta da aikin injiniya, illa dai komai ya shafi siyasa.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa tun daga lokacin da tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’Adua yake shugaban kasa har zuwa bayan gwamnatin Obasanjo, titin gwamnatin tarayya na Aba – Ikot Ekpene yana cikin harkokin siyasa kuma gwamnatin tarayya ba ta damu da hakan ba.
Yace, “Tunanina shi ne, da gangan ne.Titin Aba-Ikot-Ekpene yana da nisan kilomita 24 kacal. A shekarar 2007, shi ne har yanzu ba’ayishi ba har zuwa shekarar 2008 aka saka shi a cikin kasafin kudi akan Naira biliyan 6.
Ya bayyana cewa ko da shi Sanata T. A. Orji ya tattauna da Akpabio kan sake gina hanyar tare da aika kudirin ga gwamnatin tarayya don dawo da kudaden, “Akpabio kawai Akwa Ibom ya kare ya karbi kudin daga gwamnatin tarayya.Haka abin yake da Umuahia – Ikot Ekpene na titin gwamnatin tarayya da Enugu – Onitsha shima dai na gwamnatin tarayya da sauransu”.sannan Sanatan ya yi tambaya, “Su waye a ma’aikatar kudi da suka ki sakin asusun?