A ci gaba da binciken da rundunar sojin ruwa ke yi kan kisan wata jami’arta da aka yi a barikin Jaji da ke jihar Kaduna, rundunar sojin ta gano makasanta, inda wani saurayin mai suna Mista Simon Bernard kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito ta ce yana daga ciki.
Mista Simon Bernard wanda Malamin ne a makarantar Sakandare na sojin ruwa ne da ke cikin barikin Jaji da ita
Marigariyar ke shugabanta ya amsa laifin kashe marigariyar sakamakon sauke shi da tasa aka yi daga matsayinsa na shugaban gudanarwa na makarantar bayan wata takaddama da ya shiga tsakaninsu.
Bernard ya ce, ta yi alkawarin za a biya naira miliyan 2.5 bayan da tasa aka sauke shi a matsayinta na babba amma ba a biya shi ba, dalilin haka yasa aka kasheta.
A ranar Jumu’ar da ta gabata ne aka bayyana bacewar marigayiyar, mazauniyar Jaji, kuma tabbatar da bacewar ta bayan da ba a ganta a wajen aiki ba a ranar Litinin.
Rundunar sojin ruwa a bincikenta ne, ta kama masu yi mata aiki wanda suka jagoranci manyan sojoji zuwa rijiyar da aka jibge gawar sojar, inda aka daddatsa jikin marigayiyar tare da saka ta a cikin wata babbar jaka kafin su wulla ta a cikin rijiyar.
A ci gaban binciken ne aka kama saurayinta wanda ya amsa laifin jagorantar kisan.