Rahotanni daga Babbar Hanyar Jahar Kaduna zuwa Abuja, na cewa ‘yan Bindiga Masu Sace Mutane sun Dawo Hanyar A dazun nan da Misalin karfe 3:00pm Inda suka Budewa Motoci sama da 15 Wuta.
Bayanai dai sun ce a dazun nan ne Maharan suka Fito kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja adaidai Kauyen Kurmin Kare dake karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna.
Wani Mutum da ya Tsira daga Harin Mai suna Muhammed Danbatta, ya sheda ma Wakilinmu cewar ‘yan Bindigar sun fito daga Daji Inda suka budewa Motoci wuta, Kuma daga cikin Motocin da aka Budewa wutar har da Motar Kano, line da wata Mota kirar Jeep da aka harbi Direbanta.
Har ya zuwa Hada wannan Rahoton Babu Alkaluman Adadin Mutanen da aka Sace Ko suka ras rayukan su.