Mai ba da shawara kan harkokin siyasa, Kamfanin GIZ-SEDIN na kasar Jamus Abubakar Ahmad Gwada, ya ce adadin marasa aikin yi a Jihar Neja ya kai kashi 38.80 bisa 100, wanda ya zarce na rashin aikin yi a cikin kasar nan.
Gwada ya bayyana haka ne a wajen wani taron tattaunawa na kwana daya da gwamnati da masu zaman kansu kan magance kalubalen rashin aikin yi a jihar Neja, wanda ma’aikatar matasa da wasanni ta jihar ta shirya tare da hadin gwiwar ofishin kodineta, samar da ayyukan yi, kasuwanci da inganta sana’o’i na jihar Neja, da kuma kasa baki daya. Gami da Majalisar matasan Najeriya, reshen jihar Neja.
Ya yi kira da a kara samar da guraben kasuwanci ga mata da marasa galihu a jihar.
Masu jawabai a wajen taron sun bayar da shawarar kafa wata hukuma mai kula da ayyukan yi a jihar.
Tun da farko, Sakataren gwamnatin jihar, Ahmed Ibrahim Matane, wanda ya samu wakilcin kodinetan cibiyar ayyukan yi ta jihar Neja, Usman Magaji, ya ce gwamnatin jihar ta hada hannu da kungiyoyi masu zaman kansu, domin jawo hankalin matasa wajen koyon sana’o’i daban-daban da za su sa su zama masu dogaro da kansu.
Comments 1