Jihar Kano na da mutum 482 da suke da cutar Korona a jihar bayan da a jiya Alhamis NCDC suka tabbatar da cewa an sake samun sabbin mutum 55 da suke dauke da cutar a jihar.
Sai dai duk da wannnan adadin, har yanzu Legas ke sahun gaba wajen samun wadanda suka harbu da cutar inda yawan su ya kai 1,491, sai Kano mai 482, sai Abuja 316, Barno 125, Gombe 109, Katsina 106, Bauchi 102, Ogun 100, Kaduna 90, Sokoto 89, Jigawa 83, sai kuma Edo da Zamfara 65-65.
NCDC sun ce adadin mutanen da suka kamu da cutar Korona a jiya Alhamis sun kai 381 adadi mafi girma da aka taba gani tun bayan barkewar cutar a Nijeriya, abin da ya kawo adadin kasar zuwa 3,526, inda 601 suka warke, 107 kuma suka mutu.
Adadin da hukumar dakile cututtuka masu yaduwa a Nijeriya ta bayar a daren jiya sun nuna cewar an samu mutane 381 da suka kamu da cutar a Jihohi 18.
Sabbin Alkaluman sun nuna Legas na da mutane 183, Kano 55, Jigawa 44, Zamfara da Bauchi 19-19, Katsina 11, Borno 9, kwara 8, Kaduna 7, Gombe 6, Ogun 5, Sokoto 4, Oyo da Rivers 3-3, Neja 2, sannan jihohin Akwa Ibom da Inugu da Filato ke da guda-guda.