By Abbas Yakubu Yaura
Akalla masu ibada uku ne suka jikkata sakamakon fashewar wani abu a cikin wani masallaci a Kabul ranar Juma’a, a cewar hukumomin ‘yan sanda.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Kabul Khalid Zadran, ya ce an shirya fashewar ne da nufin auna masu ibada a masallacin Ayoub-e-Saber.
Da Dumi-duminsa: Shugaban Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa Sheikh Khalifa Bin Zayed Ya Rasu
Ya ce adadin wadanda suka mutu ya samo asali ne daga bayanan farko kamar yadda majiyoyin cikin gida suka ce adadin wadanda abin ya shafa na iya karuwa.
Ba a samu ƙarin cikakkun bayanai ba, gami da tushen fashewar, tun da farkon faruwar lamarin.
Ana ci gaba da kai munanan hare-hare a kasar Afganistan.
Kungiyar IS ta dauki alhakin yawancin hare-haren a ke kaiwa.
A watannin baya-bayan nan dai an kashe sama da mutane 100 a hare-haren da aka kai a Masallatai da mabiya addinai da kuma makarantu.
Wannan dai bashi ne karon farko da ake kaiwa hare hare a masallatai ana tsaka da sallar juma’a ba inda ake samun jikkatar masu ibada wanu lokacin ma harda rasa rayuka.
NAN