Gidauniyar uwar gidan shugaban kasa da aka fi sani da Aisha Buhari Foundation ta raba wa majinyata 6,000 daga asibitoci 11 na jihar Kano kayan abinci.
Kakakin gidauniyar, Suleiman Haruna ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa. Ya ce wata babbar jami’arsu, Fatima Rafindadi ce ta wakilci uwar dakin shugaban kasan wajen rabon kayyayakin.
Fatima Rafidadi ta ce wannan ya na daga cikin muradun gidauniyar na tallafawa mabukata musamman wadanda suke kan gadon asibiti.
Rafindadi ta nemi ‘yan Nijeriya da su taimakawa marasa lafiya musamman wadanda basu da halin biyan kudin asibiti da na abinci.
Da yake magana a madadin asibitocin, shugaban asibitin kwararru na Murtala Muhammad dake Kano, Dakta Husaini Muhammad ya yi godiya ga gidauniyar ta Aisha Buhari Foundation akan wannan aikin.
A cewarshi irin wannan kokarin zai sa wasu masu hali su ma su yunkura wajen taimaka marasa galihu.
“Asibitin nan ya fi kowanne dadewa a jihar Kano kuma yafi kowanne tara jama’a. Saboda muna samun majinyata daga wurare masu nisa. Asibitin na neman tallafi kuma wannan zai taimaka ba kadan ba. Mutane kuma suna zuwa nan ne don mafi yawan ayyukanmu kyauta ne”, inji shugaban asibitin.
Asibitocin da aka je sun hada da asibitin Hasiya Bayero, asibitin Dala, asibitin Jakara, asibitin Dawanau, asibitin Bela, asibitin Muhammad Jidda, asibitin cututtuka masu saurin yaduwa , asibitin Waziri Gidado, asibitin Abubakar Imam da asibitin Mariya Sunusi duk a cikin Kano.