Adaidai lokacin da wasu jihohi su ka sake buɗe makarantun Firamare da na Sakandire, gwamnatin tarayya ta yi kira da su ƙara yin taka-tsantsan saboda kaucewa barazanar sake ɓarkewar cutar Korona.
Tuni dai aka sake buɗe makarantun a jihohin Legas, Ekiti da kuma Ogun, yayin da wasu kuma da dama su ka saka ranakun komawar.
Sai dai gwamnatin tarayya ta yi gargaɗin cewa in ba a yi aiki da lura ba, sake buɗe makarantun, dawo da sufurin jiragen ƙasa da sauran abubuwa na iya mayar da hannun agogo baya kan irin nasarorin da yanzu haka aka samu kan yaƙi da cutar.
Sakataren gwamnatin tarayya kuma shugaban kwamitin kar-ta-kwana da shugaban ƙasa ya kafa kan yaƙi da cutar, Boss Mustapha ne ya yi gargaɗin yayin jawabin kwamitin a Abuja ranar Litinin.
Ya ce a cikin kusan mako ɗayan da ya gabata, masana ilimin kimiyya na ta ƙoƙarin gano musabbabin sake samun sabbin masu kamuwa da cutar musamman a wasu ƙasashen nahiyar turai.
https://dimokuradiyya.com.ng/korona-gwamnatin-tarayya-ta-hana-jirgin-emirates-shigowa-najeriya/
A cewarsa hakan ya sa Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta fara nuna damuwarta a kai.
Mustapha ya ce hakan ne ma ya tilasta ƙasar Isra’ila sake ƙaƙaba dokar ta tsawon makonni uku, yayin da Amurka ma ke duba yiwuwar ɗaukar makamancin wannan matakin, ƙasar Sifaniya ma ta sake sakawa a birnin Madrid duk kuwa da boren ‘yan ƙasar suka yi.
“Takamaimai darasin da Najeriya za ta koya a ciki shi ne duk da irin nasarar da mu ka samu, akwai buƙatar ƙara yin taka-tsantsan, mun buɗe tare da sassauta abubuwa da dama,” inji Mustapha.
Ya ce kiran ya zama wajibi ne la’kari da yadda a yanzu mutane ke shakulatin-ɓangaro da dokokin kiyaye yaɗuwar cutar kamar sanya takunkumi, bayar da tazara da dai sauransu.
Rahotanni dai na nuna cewa jihohi da dama na sake buɗe makarantun duk kuwa da shawarar da ake basu, ciki har da ta masana harkar lafiya kan fargabar sake barkewar cutar musamman a makarantun gwamnati saboda ƙarancin kayayyakin kariya.