Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sakkwato a ranar Alhamis ya rantsar da Alhaji Sani Garba-Shuni a matsayin shugaban ma’aikata (HOS) na jihar.
Sabon shugaban ma’aikata na jihar, kafin nada shi wannan mukamin, shi ne Sakataren ma’aikatar ayyuka da zirga-zirga na jihar.
Malam Muhammad Bello, mashawarci na musamman kan harkokin watsa labarai na gwamnan shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis din a Sakkwato.
Malam Muhammad Bello ya ce an rantsar da sabon shugaban ma’aikatar ne bayan da tsohon shugaban, Dr Buhari Bello-Kware ya yi ritaya.
Da yake jawabi a yayin rantsarwar, Gwamna Tambuwal ya taya tsohon shugaban ma’aikatar murnar kammala aikinsa cikin nasara, tare da mika godiyarsa bisa gudummawar da ya bayar a yayin gudanar da aikinsa.
Ya bayyana Bello-Kware a matsayin mutumin da ya kawo ci gaba da tsare-tsare masu amfani a bangaren ma’aikatar. Gwamna Tambuwal ya ce a lokacinsa ya sanya ma’aikata suka koyi kwamfuta tare da zama masu da’a a yayin gudanar da ayyukansu.
A cewarsa, tsohon shugaban ma’aikatar ba a same shi da aikata ba daidai ba a yayin gudanar da aikinsa.
Da yake magana kan sabon shugaban ma’aikatar, gwamnan ya ce duba da ayyukan da ya gudanar a baya, mutum ne jajirtacce akan aiki. Inda gwamnan ya taya shi murna tare da shawartarsa akan amfani da kwarewarsa da basirarsa wajen gudanar da aikin da aka dora masa.