By Abbas Yakubu Yaura
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe wani mutum da matarsa a karamar hukumar Ika ta Kudu a jihar Delta.
Shaidun gani da ido sun ce ma’auratan mai suna Chidi da Rita Edebor ‘yan bindigar sun harbe su ne a unguwar Ekwuoma-Abavo da misalin karfe 8 na daren Larabar data gabata.
Shaidun wadanda ba sa son a ambaci sunayensu, sun bayyana cewa an rika jin karar harbe-harbe daga wurin da lamarin ya faru da misalin karfe 8 na daren ranar yayin da aka tsinci Rita a bakin titi a cikin jinin inda kuma nan take aka garzaya da ita Babban asibitin Abavo, sai dai bayan kaita asibintin ne aka tabbatar ta rasu.A gefe guda kuma mijin matar Chidi ya mutu ne sakamakon harbin bindiga da ya yi masa nan take.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Wani karamin yaro dan kimanin shekara uku, wanda aka ce yana tare da wadanda lamarin ya rutsa dasu har zuwa lokacin da lamarin ya faru, bai iya bayyana abin daya faru ba sai dai ya bayyana cewa maharan biyu na dauke da makamai kuma sun sanya abin rufe fuska.
Shugaban kungiyar ‘yan kabilar Abavo, Jonathan Agbejiagwe, a lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan mamacin, ya bayyana bakin cikinsa kan lamarin wanda ya bayyana a matsayin wani bala’i daya afkawa masarautar.Ya kuma bukaci ‘yan sandan dasu kara kaimi wajen kamo masu kisan.
A halin da ake ciki, an ajiye gawarwakin wadanda aka kashe a dakin ajiyar gawa yayin da aka ce jami’an ‘yan sanda a Abavo sun fara gudanar da bincike kan lamarin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Bright Edafe, kuma mataimakin Sufurtandan ‘yan sanda, bamu samu damar jin ta bakinsa ba har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoton.