By Abbas Yakubu Yaura
Al’ummar Ibiaku Issiet da ke karamar hukumar Uruan a jihar Akwa Ibom sun rubutawa gwamnatin jihar wasika bisa zargin da suke na tafka magudin da aka yi na biyan diyya a gidan Luxury Estate na Dakkada.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Gwamnatin jihar ta mallaki yankin dake kusa da titin filin jirgin sama, Uyo daga al’umma domin gina wannan fili da makudan kudade daga cikin Naira miliyan 420 da aka riga aka biya a matsayin diyya.
Sai dai a wata takardar koke ga gwamnatin jihar ta hannun kwamishinan filaye da albarkatun ruwa, wanda wakilinmu ya samu kwafinsa a ranar Lahadin data gabata, al’ummar yankin sun bukaci a dakatar da biyan wasu kudade, bisa zargin wasu mutane kalilan ne suka yi amfani da kudaden.
Masu shigar da kara sun yi kira ga gwamnatin jihar data sake duba jerin sunayen kafin a fara biyan su, inda suka kara da cewa ba zai taba yiwuwa sunan mutum daya ya bayyana fiye da sau 132 a jerin mutane kusan guda dubu 5,625 ba.
Cif Effiong Udo, Mista Inyang Injang da Mrs Iniobong Oton ne suka sanya hannu kan takardar koken na dangin Nung Iko-Udo.
Mista Emmanuel Okon, Mista Usen Okon da Miss Arit Okon sun sanya hannu ga dangin Abak yayin da Mista Effiong Idiong da Mista Eno Idiong suka sanya hannu ga dangin Ikot Obio Etit.
“Ko da duban jerin sunayen za a iya bayyana munanan ikirari na Cif William Etim wanda sunansa ya bayyana har sau 106,da Bassey Etim shima sau 132 da Placid Etim sau 48. “Babban abin mamakin shi ne wadannan mutane da aka gano da kuma danginsu na Ekpuk (iyalinsu) basu da wani katafaren fili a yankin da ake biyan diyyar kudin.”
Da yake mayar da martani, wani tsohon dan majalisar wakilai kuma daya daga cikin wadanda ake tuhuma, Bassey Etim, yace diyyar ba wai don a biya su ne ba, sai dai ga iyalai da suke da filaye a yankin da abin ya shafa.sannan yace, “Idan gwamnati ta aika diyya, ba wai kawai ta aika kudi don mutane suje su raba wa kowa da kowa a kauyen ba. Ana bãyar da shi ga wadanda abin yashafa a cikin ƙasa.
“Ina da fili mai girman gaske wanda gwamnati bata biya ni ba, shi yasa ni kaina ban karbi ko kwabo daga cikin kudin ba a cewar sa.