Jami’in watsa labarai dake yankin Guri, Alhaji Sanusi Doro ya bayyanawa manema labarai cewa; ‘yan jihar Jigawa na bukatar agajin gaggawa duba da yadda ambaliyar ruwa ya jikkata a daminar bana. Doro ya bayyana hakan a garin Guri a ranar Alhamis. Inda ya ce wani ambaliyar sabo ya auku a daren ranar Talata.
Rahotanni daga jihar Jigawa sun tabbatar da cewa ambaliyar ruwa ya yi nasarar tarwatsa gonaki har dubu uku da gidaje 120 a garin Zuwo dake karamar hukumar Guri a jihar Jigawa. Doro ya kara da cewa; ambaliyar ruwan ya yi awon gaba da hanyar Una-Zugobia inda ya dakile zirga-zirgan ababen hawa da mutane a yankin. Ya yi kira ga gwamnatin jihar da hukumar ba da agajin gaggawa ta kasa ta NEMA da su tallafa wa wadanda lamarin ya shafa da abinci da magunguna.
Doro ya ce; karamar hukumar ta Guri sun tattara matasa domin gudanar da aikin gayya na zuba kasa a cikin buhunhuna domin tattare kogin Guri daga ci gaba da afkar da ambaliyar ruwan. “akalla matasa 150 ne ke aikin zuba kasa a buhu 1, 000.” In ji shi. Ya kara da cewa; “mutane sun yi asarar gonakinsu da suka shuka masara, dawa, ridi, gero da sauran kayan abinci.” Ya tabbatar.