A jiya Juma’a ce, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika ta’aziyar jajansa ga gwamnatin takwarar shi na Jamhoriyar Niger Mohammed Bazou, al’umar kasar, bisa ambaliyar ruwa da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, da kuma lalata gidaje.
Sakwan ta’aziyyar Buhari na zuwa ne a cikin wata sanar wa da babban Mai taimmakami shi a kan kafofin yada labarai Garba Shehu ya fitar, inda ya sanya mata lakabi da ” Ta’aziyar Shugaba Buhari, na asarar da a ka yi a Jamhoriyar Niger, sanadiyar ambaliyan ruwan sama”
Shugaban kasa Buhari, Wanda ya ce, asarar da aka tabka a Jamboriyar Niger cikin kwanaki biyu, tabbas abun damuwane matuka, inda kuma ya jajanta musu sanadiyar ruwan sama kaman da bakin kwarya da aka samu, a awasu yankuna na kasar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamna Ganduje ya bude wa Matar shi Ofishi, don inganta mata
Ya yi nuni da cewa, irin wannan iftila’i na nuna alamu ne na sauyin yanayi da aka samu a wasu kasashen duniya baki daya, da ya hadar da Nigeria, Wanda ta ke bakin kokarin ta, na ganin ta samar da wasu matakai da zasu taimaka wajan kare afkuwar lamarin.
A karshe shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi wa wadanda su ka mutu a jamhoriyar Niger, sanadiyar ambaliyan ruwan addu’a Allah ya jikan su, da kuma fatan Allah ya bai wa iyalan su hakurin rashin da su ka yi.