Mutanen unguwar Kurna Asabe a yankin ƙaramar hukumar Ungogo a cikin birnin Kano, na cigaba da kokawa kan yadda rashin magudanar ruwan ke yi musu barazanar ambaliyar ruwa.
A cewar Mazauna yankin da zarar sun ga haɗari ba su da kwanciyar hankali sakamakon fargabar ambaliyar ruwa da suke tsinci kansu a ciki.
Sun kuma ce, a duk lokacin da aka yi mamakon ruwan sama layukan unguwar na cika da ruwa, wanda ke tilastawa ruwan shiga gidajen su har ya haddasa rushe gidaje, ya yin da wasu kuma ke tafka asarar dukiya.
Wasu mazauna yankin sun shaidawa wakilinmu, “Magudanan ruwan mahaɗa ce da unguwanni kusan guda huɗu kasancewar hakan ya haifar da ƙarancin su.
Mun yi ƙoƙarin ji ta bakin hukumar tsara birane ta jihar Kano KNUPDA amma hakar mu bata cimma ruwa ba, inda jami’i hulɗa da jama’a na maikatar ya bayyana mana cewa, Shugaban hukumar ya yi tafiya akan haka ne muka tuntuɓe shi ta wayar amma wayar sa bata shiga ba.