Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje 350 da kayan abinci a wasu unguwanni uku da ke karamar hukumar Tangaza ta jihar Sokoto.
Kakakin hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, Abubakar Ghani, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mutane da dama sun rasa matsuguni a yankin.
Ya ce lamarin ya faru ne a karshen mako, inda ya ce kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da Shiyar Ajiya, Makers da kuma Runji.
Mai baiwa gwamna shawara na musamman Aminu Tambuwal wanda shine shugaban hukumar Alhaji Zabairu Magaji yace gidaje 250 ne suka lalata a kauyukan uku.
Gara Sun Cinye Takaddun Da Ke Dauke Da Bayanan Yadda Muka Kashe Naira Billiyan 17 — Hukumar NSITF
Ya yi nuni da cewa, ba a samu asarar rai ba a lokacin ifti’la’in amma ambaliyar ruwan ta tafi da kayan abinci da dama.
Ya jajanta wa al’ummar yankin tare da ba su tabbacin gwamnatin jihar za ta samar musu da kayayyakin agaji cikin gaggawa.
Mataimakin shugaban karamar hukumar, Ibrahim Lawal, ya yabawa gwamnatin jihar kan yadda ta gano mutanen da lamarin ya shafa a cikin kankanin lokaci.
Ya kuma yi kira da a samar da kayan agaji a kan lokaci ga wadanda abin ya shafa, inda kuma ya kara da cewa, da yawa daga cikinsu sun rasa matsuguni ba tare da abincin da za su ci ba.