Ministan shari’a na Nijeriya Abubakar Malami ya ce gwamnati ta karbi sama da dala miliyan 311 daga Amurka daga cikin kudaden da ake zargin tsohon shugaban mulkin soja Sani Abacha ya sace.
A wata sanarwa da maitaimaka masa kan yada labarai Dakta Umar Jibril Gwandu ya fitar ranar Litinin, ya ce kudin ruwa ya sa kudaden sun karu daga dala miliyan Dala 308 zuwa dala miliyan Dala 311 daga watan Fabrairun 2020 da aka ajiye su a babban bankin Nijeriya zuwa 28 ga Afrilu.
Sanarwar ta ce tun 2014 gwamnatin Nijeriya ta fara bin matakai na dawo da kudaden da ake kira “Abacha III.”