Akalla jami’an ‘yan sanda biyu ne aka tabbatar da mutuwar su a wata arangama tsakanin Yan sanda da jami’an sojin Najeriya a jihar Taraba.
Sojoji sun kutsa cikin hedikwatar ‘yan sandan domin ramuwar gayya kan zargin daba wa jami’insu wuka da ‘yan sanda suka yi tare da harbin ‘yan sanda kusan uku.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
Shaidun gani da ido a wurin da lamarin ya faru sun ce sojojin sun fito ne daga titin da ke zuwa hedikwatar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wurin da ake gudanar da tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Taraba, inda suka fara harbe-harbe tare da fasa tayoyin motoci.
Da ganin arangamar, jami’an ‘yan sandan da ke bakin aiki sun yi ta harbi sama.
“Ina sayar da abinci a nan hedkwatar ‘yan sanda, sai kwatsam muka ga sojoji sun fara harbe-harbe, sai muka gudu don ceton rayukan mu,” in ji magidancin mai suna Punarimam Ibrahim.
“Mun ga wani jami’in dan sanda a cikin cikin jini. Ban sani ba ko zai tsira ko a’a. Ban yi tsammanin zan tsira daga wannan lamari ba; Na ji rauni.”
Gidan Talabijin na Channels ya tattaro cewa an harbi motocin da suka hada da ayarin kwamishinan ‘yan sandan tare da tarwatsa su a harabar hedikwatar ‘yan sanda da ke Jalingo.
A lokacin da suka kai ziyara hedikwatar ‘yan sandan, an ga harsasai, da fasassun tayoyi, da lalatattun motoci tare da jami’an ‘yan sanda saboda fargabar abin da ya same su daga rundunar sojojin Nijeriya.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Abdullahi Usman, ya shaidawa majiyar Dinokuradiyya cewa an kashe jami’an rundunar biyu tare da jikkata wasu da dama.
A wani labari kuma, Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
Gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi, ya kori mambobin wasu hukumomi mallakar jihar, da kwamitoci da ko’odinetocin cibiyoyi 64 na jihar.
An umurci mutanen da abin ya shafa da su mika dukkan kadarorin gwamnati da suka hada da motocinsu na hukuma da ke hannunsu a yau ko kuma kafin rufe ofishi a ranar Litinin din nan