Wakilinmu Shu’aibu Ibrahim Gusau
Kwamishinan ‘yansanda na jihar zamfara, CP Usman Nagogo, ya baiwa shuwagabannin fulani, da Ardo Ardo, da shuwagabannin Miyati Allah, mako biyu domin dakatar da hare hare a jihar zamfara.
Kwamishinan ‘yansanda yayi wannan kiran ne a wurin taron shuwagabannin na fulani yau litinin a sakatariyar jibirin Bala Yakubu dake Gusau
Ya Kara da cewa Shuwagabannin fulani dasu jawo Yaran Nan masu kashe kashe don kawo karshen abinda yake faruwa.
CP Usman yace sun Sami korafi daga ‘yan Sakai cewa a wancen lokaci abaya da akayi sulhu ,’yanbanga da ‘yansakai sun bada makamansu har bindiga Dubu Tara (9000),Amma fulani har yanzu Basu bada nasu ba. Ya Kara da cewa daga yau an ja layi kan kisan fulani a jihar zamfara.
A nasa jawabin shugaban miyati Allah na jihar zamfara, Alhaji Ahmad Matawallen Tudun wada, ya bada umurnin rushe duk wani shugaba na kungiyar fulani kowane iri a jihar zamfara,ya ce kowa ya jira sai an nada sabbin shuwagabanni.