A dalilin hukuncin kotu da na dakatar da shugaban jam’iyyar APC Adams Oshiomhole daga ci gaba da jagorancin jam’iyyar, kamar yadda wata babban kotu ta yanke tun farko, jam’iyyar APC ta nada Sanata Abiola Ajimobi, tsohon gwamnan jihar Oyo, a matsayin shugaban shugaban jam’iyyar APC na wucin-gadi har sai kammala shari’ar da aka shigar a gabanta.
Kakakin jam’iyyar APC, Mal Lanre Issa-Onilu ya ce dokar jam’iyyar ta ba mataimakin jam’iyyar na shiyyar Kudu damar darewa kujerar shugabancin jam’iyyar na wucin gadi a lokacin da aka samu gibi a kujerar shugabancin jam’iyyar.
Sanata Ajimobi, sirikin gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje ne mataimakin shugaban jam’iyyar na shiyyar Kudu.
cikin hukuncin da kotun ta yanke, har jami’an tsaron dake kare shi duk an janye su. Kotu tace kotun baya ta yi daidai a hukuncinta. Ta kuma yi watsi da korafin da Oshiomhole ya mika gabanta.
Idan ba a manta ba kotun a Abuja ta dakatar da Oshiomhole daga ci gaba da bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar APC a watan Maris.
Wanda ya shigar da karar Lauya Afolabi ya ce babbar hujjarsu na shigar da kara shi ne a dakatar da Oshiomhole daga jam’iyyar.
Yace hakan ya tabbatar da Oshiomhole ba dan jam’iyya ban a yanzu saboda haka bai cancanci ci gaba da zama a kujerar shugabancin jam’iyyar ba.
Oshiomhole ya garzaya kotun daukaka kara domin kalubalantar wannan hukunci da kotu ta yi da kuma garkame ofishin jam’iyyar da hukumomin tsaro suka yi, domin yin biyayya ga hukuncin kotun.