Tsohon jami’in leken asiri na rundunar soja, Kanar Hassan Stan-Labo (rtd) ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tura jiragen yaki marasa matuka a fadin kasar nan.
Najeriya dai na fama da matsalolin tsaro da suka hada da ‘yan fashin daji da masu ta’addanci, garkuwa da mutane, tsageru, kiraye-kirayen ballewa da dai sauransu.
A yankin Arewa-maso-Yamma, Kaduna, Katsina, Zamfara, Sokoto da Kebbi, an sha fama da hare-haren kungiyoyin ta’addanci.
Daruruwan mutane ne aka kashe ko kuma yin garkuwa da wasu a Katsina cikin wannan shekara tare da raba wasu dubbai daga gidajensu.
Amma da yake magana yayin wata hira da gidan talabijin na Channels a shirin Sunrise Daily, Stan-Labo ya ce fasaha ba ta taka rawar da ake bukata a yankin Arewa maso Gabas.
“Mene ne jirage marasa matuka saboda Kristi? Ya zuwa yanzu, ya kamata waɗannan abubuwa su kasance a ko’ina. Ina mamakin mene ne ya hana mu daukar wasu daga cikin wadannan matakan. A yau muna da manyan jirage marasa matuka a kasuwa wadanda za su gudanar da ayyukan sa ido,” in ji shi.
“Abin da kawai kuke buƙata shine ku zauna a ɗakin aikin ba da umarni, danna madanni kuma jirage marasa matuka za su shagaltu da yin duk ayyukan aika da za a sami sakamako da sauransu. A yanzu ya kamata mu shiga aiki da jiragen marasa matuka.”
Jami’in soja mai ritaya ya kuma yi kira da a kara samar da tallafi ga masu yi wa kasa hidima, inda ya ce samun albashi mai tsoka zai kara kwarin gwiwa ga rundunar.
Bugu da kari, yana son gwamnati ta yi la’akari da halin da jami’an da suka yi kokarin yi wa kasa hidima sai a yi watsi da su bayan sun yi ritaya.
A cewarsa, gwamnatin da ke ci a yanzu ba ta yi wani abin a zo a gani ba wajen habaka ma’aikata a fannin gine-ginen tsaron kasar nan.
“Me ya sa har yanzu muke jinkirta duk wani abu da ya kamata mu yi dangane da inganta ma’aikata a fannin tsaro duba da jami’an tsaro da ma ‘yan sanda?
“Har yanzu ban ga wani matakin gaggawa da wannan gwamnati ta yi don ganin mun inganta aikin dan adam ba. Ma’aikata sun zama babbar matsala a gare mu a aikin soja, haka nan ‘yan sanda,” ya kara da cewa.