A wani yunƙuri na ƙarfafa ƙarfin aiki ga jami’an tsaro na ‘yan sanda da ke shiga wurare daban daban domin gudanar da ayyuka a faɗin jihar, a jiya Laraba Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara CP Ayuba N. Elkanah psc+ ya fara ziyarar gani da ido zuwa wuraren da aka tura jami’an ‘yan sanda da ke aiki da rundunar Operation Puff Adder a yankin Gusau zuwa Mayanci zuwa Maradun da Talata Mafara da Bakura.
Makasudin ziyarar shi ne don tantance iya aiki da kuma yin gyare-gyaren da ya dace wanda zai inganta aikin jami’an.
A yayin ziyarar aikin, Kwamishinan ‘yan sandan ya umarci jami’an da su kasance masu kwarewa a cikin ayyukansu. Ya kuma bukace su da su kula da lafiyarsu da muhimmanci sosai domin a samar wa al’umma kariya daga ayyukan ‘yan fashi da makami da sauran miyagun laifuka.
Mai magana da yawun Rundunar SP Muhammad Shehu cikin wata sanarwa da ya aikowa da jaridar Dimokuraɗiyya ya bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sandan ya kuma yaba da jajircewar jami’an ‘yan sandan. Inda kuma ya umarce su da su ci gaba da zama jakadu nagari, ta hanyar aiki tukuru da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu, tare da inganta hadin gwiwarsu da sauran jami’an tsaro da sauran al’ummomin da suka karbi bakuncinsu.
Kwamishinan ya tabbatar musu da cewa Sufeto Janar na ‘yan sanda IGP Alkali Usman Baba psc+, NPM, fdc yana sane da jajircewarsu wajen gudanar da ayyukan yaki da masu aikata laifuka, ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu yayin da Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, da tawagarsa ke ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da tsaro a yankin.