Ana ci gaba da yin suka daga ‘yan Najeriya kan shirin gwamnatin tarayya na haramta kungiyar malaman jami’o’i (ASUU).
Rahotanni sun bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na shirin rushe kungiyar malaman jami’o’in Najeriya ASUU saboda gazawarta na janye yajin aikin da ta dauki tsawon lokaci tana yi bayan wasu tayi da gwamnatin tayi kungiyar ta yi watsi da su.
Wasu ‘yan Najeriya a shafukan sada zumunta sun bayyana shirin a matsayin na gaggawa, inda suka nemi gwamnatin tarayya ta sake tunani kan irin wannan shirin.
Karanta kuma: Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya Na Shirin Haramta Kungiyar ASUU
Wasu kuma sun ce matakin ne da bai dace ba wanda zai iya haifar da mummunan sakamako fiye da yadda kasar ke fama da shi a halin yanzu.
Wani mai amfani da Twitter @NsikakAnietie ya ce “Gajeren mataki a lokaci babbar Matsala. Hakan zai sa makarantun gwamnatin tarayya su bude kasa baki daya amma lalacewar fannin ilimi a NIGERIA zai zama abin da ba a taba ganin irinsa ba a duk fadin duniya.”
Wani mai amfanin shima @Abskilz1 ya ce haramcin “ba zai zama alheri ba. Daga kwanon soya zuwa wuta… Gwamnati har yanzu tana tilasta wa ASUU bukata. Yakamata kawai su biya bashin su. Dalibai ne za su yi asara. Daga ƙarshe bayan waɗannan ɓata lokaci, har yanzu za su biya su. Haramtawa?? Nahh.”
A nasa bangaren, @Olusegun_saint, ya ce tamkar zuba man fetur ne a kan wuta, ya kara da cewa “mutane da yawa za ta cinye. Hakan kuma zai shafi sakamakon zaben da ke tafe. Shin muna tare da iyawar tunaninmu?”, jaridar Vanguard ce ta rawaito labarin.
A wani kuma labarin: Yajin Aiki: Malaman Makaranta Suna Koma Noma, Da Wasu Ayyukan — Shugaban ASUU
Kungiyar malaman jami’o’i ta bayyana cewa malaman jami’o’in sun zabi yin wasu ayyukan da ba na ilimi ba domin samun rayuwa sakamakon yajin aikin da ta ke yi, a cewar gidan talabijin na channels.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, ASUU dai ta shiga yajin aikin ne tun ranar 14 ga watan Fabrairu saboda inganta walwala, farfado da jami’o’in gwamnati da cin gashin kansu na ilimi da dai sauran bukatu.