By Abbas Yakubu Yaura
An kama wani sajan na rundunar sojin sama bisa zarginsa da hannu a harin da aka kai makarantar horas da sojoji ta Najeriya (NDA) dake jihar Kaduna.
Rahotanni sun bayyana cewa an kama Sajan Torsabo Solomon ne a ranar Litinin din data gabata bisa umarnin kwamandan Base, 153 BSG Yola dake jihar Adamawa, biyo bayan bukatar da hukumomin soji a Kaduna suka yi.
Wadanda suka shaida lamarin sun ce an dauke sajan din dake Makarantar Komprehensive na Sojan Sama da ke Yola zuwa Kaduna a cikin jirgin Soja mai lamba NAF 930 da karfe 8:15 na safe domin ci gaba da yi masa tambayoyi kan batun makamai da alburusai da aka yi amfani dasu a harin Kadunan NDA.
Da wakilinmu ya tuntubi kakakin rundunar ta 153, Lieutenant Bayem ya ki cewa komai, inda yace zai sake kiransa.
Sai dai wasu majiyoyi a sansanin sojin sama sun tabbatar da kamun, inda suka ce labarin shigar wanda ake zargin a irin wannan aika aika ya girgiza jami’ai da mazan dake cikin aikin sojan.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa ‘Yan bindiga sun kai hari a NDA a watan Agusta, inda suka kashe sojoji biyu tare da yin garkuwa da wani, lamarin da ya girgiza al’ummar kasar.