Daga Abdullahi Kebbi
Bisa ga rahotannin da ke fitowa daga jamhuriyar kamaru na nunarda cewa an kaiwa ‘yan awaren kasar kamaru hari tare da kashe Mutane 17 daga cikinsu.
A wata sanarwa da rundunar sojin kasar Kamaru ta fitar ta bayyana cewa sojojin kwantar da tarzoma sun kai hari a kauyen Bali da nufin kwantar da tarzomar.
Sai dai dakarun na kwantarda tarzoma sun kashe ‘yan awaren 17 tare da kwace wasu makamai daga hannun su.
Sai dai wannan hari bai shafi farar hula ko daya ba.