Hukumar tsaron Fararan Hula da kare kaddarorin Gwamnati ta Najeriya NSCDC ta bayyana cewa, an kama wasu mutane hudu da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihar Sokoto.
Rahotanni sun nuna cewa, wadanda ake zargin ‘ya’yan wata fitacciyar kungiyar ‘yan bindiga ne da ke aiki a jihohin Sokoto da Zamfara.
An kuma gurfanar da su ne bisa zarginsu da hannu a manyan aikukan garkuwa da mutane, fashi da makami, da satar shanu, da kisan kai a tsakanin al’ummomin jihohin Arewa maso Yamma biyu.
Kwamandan Hukumar ta NSCDC a shiyar Jihar Sakkwato, Mohammed Saleh-Dada, ya ce wasu daga cikin wadanda aka kama suma masu bai wa ‘yan bindiga bayanan sirri ne kan wasu manyan hare-haren da aka kai a yankin.
KSRANTA WANNAN LABARIN: Yan bindiga sun hallaka Mutane 11 A Jihar Katsina
Ya Kuma kara da cewa, an gayyaci wani babban jigo a karamar hukumar Dange/Shuni a jihar Sokoto, saboda alakarsa da daya daga cikin wadanda ake zargin.
“Har ila yau, an kama wani wanda ake zargi da yin lalata da wasu Almajirai sama da 12 a jihar Sokoto” inji shi
Comments 1