Jami’an tsaro a Jihar Osun sun cafke wani dan kungiyar Yarbawa ta Oduduwa bisa zargin sace wata matashiya mai shekara 20 inda ya yi mata yankan rago tare da yin tsafi da sassan jikin ta.
Kwamishinan yan sandar Jihar CP Wale Olokode shi ya tabbatar da hakan yayin da yake gabatar da mutumin dan shekara 40 mai suna Kabiru Oyetuntan ga manema labarai a yammacin jiya.
CP Wale Olokode ya ce mutumin wanda dan asalin kauyen Moninun ne an yi nasarar cafke shi ne a unguwar Quarry dake yankin Apomu biyo bayan wasu bayanan sirri da rundunar yan sandar jihar ta samu.
Sai dai kuma Kabiru Oyeduntan ya musanta zargin da ake masa inda ya ce atafau abokinsa ne ke da alhakin wannan aika-aika.
Yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutumin inda za a gurfanar da shi a gaban kotu da zarar an kammala, kamar yadda Kwamishinan yan sandar ya bayyana.