Rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta kama wani matashi dan shekara 28 mai suna Ismail Adewuyi, da aka same shi da kan wata mata da kuma hanji a yankin Ede da ke jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Yemisi Opalola ta bayyana haka a Osogbo inda ya kara da cewa, an kama wanda ake zargi da aikata tsafi a ranar Asabar a hannun wani dan kungiyar mafarauta ta Najeriya, Isa Usman, wanda ya kai shi wurin ‘yan sanda.
KARANTA KUMA: Yan Sanda Sun Kama Mutane Uku Da Kokon Kan Mutum
Ta kara da cewa mafaraucin ya kama Adewuyi a kusa da wata makabarta.
Kamfanin dillacin labarai na kasa NAN ya rawaito cewa, Opalola ta kuma bayyana cewa ‘yan sanda sun fara yiwa wanda ake zargin tambayoyi. (NAN)
A wani labarin kuma: Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Bukaci FG Ta Gaggauta Aiwatar Da Aiki Mambilla
Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas (NEGF) ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta aiwatar da aikin samar da wutar lantarki na Mambilla a jihar Taraba.
Sun yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwar da suka fitar a karshen taron su na bakwai da suka gudanar a karshen mako a gidan gwamnatin Gombe a jihar.
Comments 1